Friday, May 8
Shadow

Duk Labarai

Sarakunan Inyamurai sun ce Tinubu ne zabinsu a 2027

Sarakunan Inyamurai sun ce Tinubu ne zabinsu a 2027

Duk Labarai
Sarakunan yankin Inyamurai sun yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu alkawarin samar masa akalla kaso 70 cikin 100 na kuri'un da za'a kada a yankunansu. Sarakunan wanda basaraken Abia, Eze Nnamdi yake jagoranta sun bayyana hakane yayin da suka kaiwa mataimakin kakakin majalisar dattijai, Benjamin Kalu ziyara a gidansa dake Abia Sunce babban dalilin ziyararsu shine dan mika godiya ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bisa kafa ma'aikatar raya yankinsu. Sannan sun kuma Godewa Sanata Kalu saboda kokarin da yayi na kafa wannan ma'aikata.
Ji Yadda ma’aikacin banki ya riƙa naɗar bidiyon tsìraìcìn abokan aikinsa mata a Najeriya, ya nadi Bidiyo 400

Ji Yadda ma’aikacin banki ya riƙa naɗar bidiyon tsìraìcìn abokan aikinsa mata a Najeriya, ya nadi Bidiyo 400

Duk Labarai
Yadda ma'aikacin banki ya riƙa naɗar bidiyon tsiraicin abokan aikinsa mata a Najeriya. Rundunar ƴansanda a jihar Legas da ke Najeriya ta ce za ta gurfanar da tsophon ma'aikacin bankin Access wanda ake zargi da ɗaukar hotunan tsiraicin abokan aikinsa mata. Wannan na zuwa ne bayan wata sanarwa da bankin ya fitar a ranar Litinin inda ya bayyana cewa ya miƙa batun zargin ɗaya daga cikin ma'aikatansu a ɓangaren hulɗa da abokan cinikayya, na ɗaukar hotunan tsiraici ga hukumomi. Sanarwar da suka wallafa a shafin sada zumunta ta ce bankin zai bai wa hukumomi haɗin kai, kuma bankin zai ci gaba da kare mutuncin ma'aikatansa. Bayani da ya fita a makon da ya gabata ya nuna cewa wani ma'aikacin bankin Access ya naɗi bidiyoyin abokan aikinsa mata a cikin ban-ɗaki ba tare da saninsu ba....
Kalli Bidiyo: Bayan ya bayar da hakuri kan bidiyonsa da aka gani yana rabawa ‘yansanda kudi, An kuma kara ganin dan Chinar nan yana watsawa ma’aikatansa kudi a wajan hakar ma’adanai

Kalli Bidiyo: Bayan ya bayar da hakuri kan bidiyonsa da aka gani yana rabawa ‘yansanda kudi, An kuma kara ganin dan Chinar nan yana watsawa ma’aikatansa kudi a wajan hakar ma’adanai

Duk Labarai
Dan kasar Chinar nan da kwanakin baya aka ganshi a wani Bidiyo da ya yadu sosai yana rabawa 'yansandan Najeriya kudi wanda har daga baya ya fito ya bada hakiri, ya sake aikata laifin. A wannan karin, ganinsa aka yi yana watsawa ma'aikatansa kudi a kasa suna rububi a wajan hakar ma'adanai. https://twitter.com/thecableng/status/1916889365088784551?t=4ZnGGNlAc-i4iQe5INZGVw&s=19 Wannan dai cin zarafin Naira ne kamar yanda hukumar EFCC ta Haramta yin hakan. Abin jira a gani shine wane hukunci ne hukumomi zasu dauka a kansa.
Ji yanda ta kaya bayan da Na Yi Ido Biyu Da Wanda Suka Yi Gàrkùwà Da Ni A Masallacin garin mu, inji Cmr. Mb Muhammad

Ji yanda ta kaya bayan da Na Yi Ido Biyu Da Wanda Suka Yi Gàrkùwà Da Ni A Masallacin garin mu, inji Cmr. Mb Muhammad

Duk Labarai
Yadda Na Yi Ido Biyu Da Wanda Suka Yi Garkuwa Da Ni A Masallaci, inji Cmr. Mb Muhammad. "Na yi alwala zan yi Sallah a gidan man Shema dake Bakin Ruwa Kaduna, sai na ga daya daga cikin wadanda suka yi garkuwa da ni a masallacin shi ma zai yi sallah. Bayan mun idar a Salla sai na tambaye shi ka gane ni? Yace eh ya gane ni, amma yanzu amma yanzu na tuba na daina wannan mummunar harkar ta ta'aďdancin, yanzu haka ma sana'ar acaba nake yi don na rufawa kaina da iyalina asiri. Sauran abokanan sana'ar mu wasu an kashe su wasu kuma sun tuba inji shi dan ta'aďdan, daga karshe na ce na yafe masa kuma na yi masa alkairi". Shin idan kai ne za ka yafe masa? Daga Madubi H
Ina Son In Sanar Al’ummar Jihar Katsina Da Ku Cewar “Shugaban Kasa Bola Tinubu Zai Zo Jihar Katsina Kuma Ya Kwana, Wanda Bai Taɓa Yi Ba A Cikin Jihohin Najeriya, Bayan Mahaifarsa Jihar Legas, Domin Taya Mu Murna Da Kuma Ƙaddamar Da Ayyuka. Ina Kira Ga Al’ummar Jihar Katsina Su Fito Tarbar Shugaban Kasa”.

Ina Son In Sanar Al’ummar Jihar Katsina Da Ku Cewar “Shugaban Kasa Bola Tinubu Zai Zo Jihar Katsina Kuma Ya Kwana, Wanda Bai Taɓa Yi Ba A Cikin Jihohin Najeriya, Bayan Mahaifarsa Jihar Legas, Domin Taya Mu Murna Da Kuma Ƙaddamar Da Ayyuka. Ina Kira Ga Al’ummar Jihar Katsina Su Fito Tarbar Shugaban Kasa”.

Duk Labarai
Jihar Katsina Za Ta Zama Jiha Ta Farko A Cikin Jihohin Nijeriya Da Shugaba Tinubu Zai Zo Ya Kwana Tun Bayan Rantsar Da Shi, Banda Legas, Cewar Gwamna Dikko Radda Ina Son In Sanar Al'ummar Jihar Katsina Da Ku Cewar "Shugaban Kasa Bola Tinubu Zai Zo Jihar Katsina Kuma Ya Kwana, Wanda Bai Taɓa Yi Ba A Cikin Jihohin Najeriya, Bayan Mahaifarsa Jihar Legas, Domin Taya Mu Murna Da Kuma Ƙaddamar Da Ayyuka. Ina Kira Ga Al'ummar Jihar Katsina Su Fito Tarbar Shugaban Kasa". Daga Jamilu Dabawa, Katsina
Wace Kadunar kaje? Mutanen Kaduna suna tambayi Tsohon Hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad bayan da yace ya je Kaduna yaga Gwamnatin jihar na ta aiki tukuru

Wace Kadunar kaje? Mutanen Kaduna suna tambayi Tsohon Hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad bayan da yace ya je Kaduna yaga Gwamnatin jihar na ta aiki tukuru

Duk Labarai
Hadimin tsohon shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad ya wallafa a shafinsa na sada zumunta cewa ya je Kaduna a karshen mako kuma yaga yanda Gwamnatin jihar ke ta ayyukan raya kasa. Yace irin abinda suke nema a Kano kenan tun shekara 1999. https://twitter.com/BashirAhmaad/status/1916925432441753937?t=-the03HnWAK_hcUAUnd99Q&s=19 Saidai 'yan Kaduna da yawa sun yi caaa a kansa inda suke tambayar shi cewa wace Kadunar ya je?
SDP ta fara kaɗa hantar jam’iyya mai mulki, mu ba gwaskaye mu ke so ba Talakawa sun ishe mu – El-Rufai

SDP ta fara kaɗa hantar jam’iyya mai mulki, mu ba gwaskaye mu ke so ba Talakawa sun ishe mu – El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya ce sabuwar jam’iyyar da ya koma, SDP, ta fi buƙatar ta tara mambobi daga tushe ba wai manyan ƴan siyasa ba. El-Rufai, wanda ya fice da ga jam’iyyar APC a watannin baya, ya baiyana hakan ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudanar a jihar Kano a yau Litinin. A cewar sa, SDP jam’iyya ce da ke rajin farfaɗo da dimokuraɗiyya tun daga tushe domin gyaran Nijeriya. “Mu ba mu damu da tara manyan ƴan siyasa a SDP ba. Mun fi son mu ga kamar mutane miliyan 3 sun yi rijista a SDP. “SDP jam’iyya ce da za ta baiwa kowa dama iri ɗaya. Ba za mu bari wani mutum ɗaya ya riƙa iko da jam’iyyar ba. “So mu ke yi mu gyara dimokuraɗiyyar kasar nan,” in ji El-Rufai, yayin da ya ke amsa tambayoyi daga manema labarai. Hakazalika El-Rufai ya ce...
Miliyoyin mutane a kasashen Sifaniya da Portugal sun tsinci kansu cikin yanayi na duhu sakamakon katsewar lantarki a sassan ƙasashen

Miliyoyin mutane a kasashen Sifaniya da Portugal sun tsinci kansu cikin yanayi na duhu sakamakon katsewar lantarki a sassan ƙasashen

Duk Labarai
Miliyoyin mutane a kasashen Sifaniya da Portugal sun tsinci kansu cikin yanayi na duhu sakamakon katsewar lantarki a sassan ƙasashen. Lamarin ya shafi harkokin sufuri da sadarwa, da ma harkokin kasuwanci da dama. Asibitoci na gudanar da harkokinsu yadda aka saba saboda suna amfani da injinan janareto. Reuters