Wednesday, July 1
Shadow

Duk Labarai

Rikicin Aminu J Twon, Ordinary President da matar soja, Waye me gaskiya?

Rikicin Aminu J Twon, Ordinary President da matar soja, Waye me gaskiya?

Duk Labarai
Matar soja Seaman Haruna Abbas ta dauki zafi sosai akan neman taimakon da Aminu J. Town yace ya mata inda ta yi ikirarin cewa ba da saninta bane. Hakanan Shima Ordinary President, Ahmad Isah wanda ta je gidan talabijin da rediyonsa wajan neman hakkin mijinta, ya dauki zafi duk da dai yawa Aminu J. Town Nasiha. Hakanan a bangaren Aminu J. Town, shima bai dauki abin da sauki ba inda yayi zargin cewa ana son bata masa suna. Aminu J. Town dai ya bayyana cewa an nemi ya tarawa matar sojan ruwa, Seaman Haruna Abbas wadda ta kai kara gidan talabijin na Ordinary president inda tace an tsareshi tsawon shekaru 6 ba tare da hukunci ba kan zargin yayi yunkurin kashe ogansa. J Town yace yayi kokarin neman lambar matar inda ya kira dan neman izinin tara mata taimakon. Ga bidiyon wayar da ...
Wahala ta yi yawa, A tausayawa Talakawa>>Tsohon Shugaban kasa,Abdulsalam Abubakar ya roki Gwammati

Wahala ta yi yawa, A tausayawa Talakawa>>Tsohon Shugaban kasa,Abdulsalam Abubakar ya roki Gwammati

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa,Abdulsalam Abubakar ya gayawa Gwamnati cewa wahalar da ake ciki a kasarnan ta yi yawa. Ya bayyanawa manema labarai cewa,mutane da yawa a yanzu basu da kudi inda kudin mota da sauran ababen hawa suka karu ga kudin makarantar yara ya karu kuma mutane basa iya cin abinci sau 3 a rana. Yace shi da wasu masu fada a ji sun baiwa gwamnatin tarayya shawarar yanda za'a fita daga cikin halin da ake ciki. Daya daga cikin hanyoyin kamar yanda yace sune gwamnatin ta sayi abinci ta rika sayarwa a farashi me sauki. Ya kuma bayar da shawara ga masu shirin yin zanga-zangar tsadar rayuwa ta ranar 1 ga wata October da kada a tayar da hankali a yi ta cikin lumana.
Najeriya Za ta Zama Jagorar Kasuwar Halal Ta Duniya Mai Jarin Dala Bilyan Dubu 7- Kashim Shettima

Najeriya Za ta Zama Jagorar Kasuwar Halal Ta Duniya Mai Jarin Dala Bilyan Dubu 7- Kashim Shettima

Duk Labarai
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bayyana cewa Najeriya na kan gaba a fannin tattalin arziki ta bangaren Kasuwar Musulmi zalla da ake kira da Kasuwar halal ta duniya, wadda aka yi hasashen jarinta zai haura Dalar Amurka tiriliyan 7.7 a shekarar 2025. Kashim ya bayyana haka ne a wajen taron masu ruwa da tsaki na tattalin arzikin Halal da aka gudanar a dakin taro na Banquet Hall dake fadar shugaban kasa a Abuja a yau Laraba, 18/09/24. Mataimakin ya jaddada cewa girman tattalin arzikin Najeriya da yawan al'ummarta yana samar mata da damammaki musamman a bangaren bunkasa sashen saka hannun jari na halal. Kasuwar Rumbun Halal wani shiri ne da ya kunshi sayar da ababen da addinin Musulunci ya halasta da suka hada da halatattun abinci da abin sha, da kayan kwalliya, da na gyara...
YANZU-YANZU: Rarara Ya Bada Kyautar Naira Miliyan Goma Ga Waɗanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

YANZU-YANZU: Rarara Ya Bada Kyautar Naira Miliyan Goma Ga Waɗanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Duk Labarai
Rarara Ya Bada Kyautar Naira Miliyan Goma Ga Waɗanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri Mawaƙi Dauda Kahutu Rarara, ya bayar da gudunmuwar Naira miliyan 10 domin a tallafawa waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri. A rahoton da Jaridar Dokin Ƙarfe TV ta samu, Rarara ya jajantawa Gwamna Babagana Zulum, Da mai martaba Shehun Barno a yayin ziyarar da Ya kai musu. Sannan Rarara ya ƙara jajantawa al’ummar jihar, musamman waɗanda suka yi asara sakamakon ambaliyar ruwan. A yayin ziyarar jajen, Rarara ya samu rakiyar Hajiya Aysha Humaira, Dak Abdullahi Al-Hikimah, Alan Waƙa, da Onarabul Auawal Ahmed Bakori da sauransu.