Tuesday, May 19
Shadow

Wahala ta yi yawa, A tausayawa Talakawa>>Tsohon Shugaban kasa,Abdulsalam Abubakar ya roki Gwammati

Tsohon shugaban kasa,Abdulsalam Abubakar ya gayawa Gwamnati cewa wahalar da ake ciki a kasarnan ta yi yawa.

Ya bayyanawa manema labarai cewa,mutane da yawa a yanzu basu da kudi inda kudin mota da sauran ababen hawa suka karu ga kudin makarantar yara ya karu kuma mutane basa iya cin abinci sau 3 a rana.

Yace shi da wasu masu fada a ji sun baiwa gwamnatin tarayya shawarar yanda za’a fita daga cikin halin da ake ciki.

Daya daga cikin hanyoyin kamar yanda yace sune gwamnatin ta sayi abinci ta rika sayarwa a farashi me sauki.

Ya kuma bayar da shawara ga masu shirin yin zanga-zangar tsadar rayuwa ta ranar 1 ga wata October da kada a tayar da hankali a yi ta cikin lumana.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Matashiya 'yar Jihar Bauchi me shekaru 19 ta na neman mijin aure me Hankali, Mahaifinta me kudi ne amma tace ita matashi indai yana da sana'a da nutsuwa zasu daidaita

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *