Wednesday, April 29
Shadow

Cewa a zabi Tinubu hade yake da cewa a zabi Kashim Shettima ko da ba’a fada ba>>Inji Tsohon Hadimin shugaban kasa, Bashir Ahmad

Tsohon Hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad ya bayyana cewa, cewa a zabi shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ko da ba’a hada da kiran sunan Kashim Shettima ba, duk yana nufin a zabesu tarene.

Ya bayyana hakane a kafar sada zumuntarsa.

Hakan na zuwane yayin da rikici ya taso a cikin jam’iyyar inda ake zargin shugaba Tinubu ba zai ci gaba da tafiya da Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa ba a zaben shekarar 2027.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Ji Abinda mataimakin Gwamnan Bauchi yace bayan da "ya zabgawa Minista mari"

A jiya dai a wajan taron nuna goyon bayan Tinubu na masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC daga Arewa maso gabas, an baiwa hammata iska bayan cewa a zabi Tinubu ba tare da kiran sunan Kashim Shettima ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *