
Rahotanni sun bayyana cewa, an jibge jami’an tsaro a ofishin INEC dake Abuja dan hana jam’iyyar ADC zanga-zanga.
Jam’iyyar ADC ta yi barazanar yin zanga-zanga kan cire sunayen shuwagabannin ta daga shafin INEC.
Dan hakane aka jibge jami’an tsaron.
An ga hotunan jami’an tsaro dauke da muggan makamai da tankokin ruwan zafi zagaye da ofishin INEC.