Wednesday, April 29
Shadow

Da Duminsa: An sake daga jana’izar Aminu Dantata

Bayanai daga makusantan marigayi Alhaji Aminu Ɗantata sun nuna cewa an ɗage jana’izar marigayin da aka shirya gudanarwa bayan sallar La’asar a ranar Talata.

Yanzu an mayar da jana’izar zuwa bayan Magariba a haramin birnin Madina.

Dama dai Mustapha Junaid, mataimaki na musamman ga marigayin ya shaida wa BBC cewa tuni gawar Alhaji Aminu ta isa birnin na Madina.

“Alhamdu lillah an ɗauki marigayi Alhaji Aminu Ɗantata daga filin jirgi na Madina kuma yanzu haka za a je Shakzura inda a nan ne za a ƙarasa shirya shi kafin daga bisani a kai shi haramin Madina domin gudanar da sallah kamar yadda hukumomin Saudiyya suka amince.” In ji Mustapha Junaid.

Karanta Wannan  Ni Musulmi ne kuma nasa Allah a raina sanda nake aiki, Na yiwa Najeriya aiki tukuru ta yanda ko hutu bana samu, kuma a shirye nake na amsa tambayoyin EFCC, amma dai yanzu basu kamani ba ina nan ina hutawa tukuna>>Tsohon Shugaban NNPCL, Mele Kolo Kyari

A ranar Asabar ne shahararren ɗankasuwa Aminu Ɗantata ya rasu yana da shekara 94 da haihuwa a shekarar miladiyya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *