
A yayin da abubuwa ke kara kamari a gabas ta tsakiya.
Rahotanni na cewa, wata baraka ta kunno kai tsakanin kasar Saudiyya da kasar Amurka.
A wata hira da wakilin kasar Saudiyya yayi da Aljazeera, ya koka da cewa qasar Amurka, ta kwashe duk wasu makamanta daka iya tare hare-hare ta sama ta kaisu kasar Israyla.
Ya koka da cewa yayin da su kuma kasashen Larabawa da suka baiwa Amurkar Sansani ta ajiye sojojinta an barsu su ji da kansu.
Saidai Hukumar tsaro ta kasar Amurka tace suna tarewa kowace kasa barazanar harin da ake kai mata a yankin Larabawan.