
Hukumar EFCC ta tabbatar da cewa, ta aikawa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sammacen ya bayyana a gabanta.
Hakan na zuwane bayan da aka yi yunkurin kamashi a filin jirgi amma abu ya faskara.
Rahotanni sun bayyana cewa, Lauyoyin EFCC ne suka tabbatar da hakan.
Kuma sun ce, ElRufai ya amsa musu da cewa, zai bayyana a gaban EFCC din ranar Litinin.