
Rahotanni daga Abuja na cewa, EFCC sun sake komawa gidan tsohon Ministan shari’a Abubakar Malami dake Abuja.
Rahotanni yace EFCC sun je gidan ne a motocin bas guda 5 inda suka kulle layin gidan na Malami sannan sun hana kowa wucewa.
A jiya ma dai EFCC sun je gidan Abubakar Malami inda suka kulle wasu gidajen sa da guraren kasuwancinsa.