
A yaune aka tashi da labarin shugaban kungiyar Dalibai ta kasa, Comrade Atiku Abubakar Isah inda ya zargi dan shugaban kasa, Seyi Tinubu da daukar nauyin ‘yan daba suka dakeshi.
Yace an masa wannan cin zarafine saboda yace ba zai goyi bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba.
Saidai a martaninsa, Dan shugaban kasar, Seyi Tinubu yace wannan zargi ba gaskiya bane.
A sakon da ya fitar ta shafinsa na Instagram, Seyi Tinubu yace shi baima taba haduwa da shugaban kungiyar dalibanba.