Friday, December 26
Shadow

Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ce Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya koma jihar Kebbi da zama har sai an kubutar da dalibai ‘yan mata

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya baiwa karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle umarnin komawa jihar Kebbi da zama har sai an kubutar da dalibai mata da aka yi Gharkùwà dasu.

Ana taammanin nan da ranar Juma’a ne Bello Matawalle zai koma jihar Kebbin da zama dan ya jagoranci kubutar da ‘yan matan.

Yara mata 25 ne dai aka sace daga makarantunsu inda kuma aka Khashye daya daga cikin malamansu

Lamarin ya jawo Allah wadai da kiraye-kirayen a dauki mataki.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Siyasa ba da gaba ba Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Dare da Ministan tsaro, Bello Matawalle na tafawa a wajan jana'izar Buhari

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *