Monday, April 27
Shadow

Daya daga cikin masu laifin da suka tsere daga gidan yari yace a aikawa mahaifiyarsa Ladar Naira Miliyan 5 da aka saka ga duk wanda ya taimaka aka kamasu shi kuma zai koma gidan yarin da kanshi

Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnati ta saka ladar Naira Miliyan 5 ga duk wanda ya taimaka aka kama wadanda suka tsere daga gidan yarin Ilesa na jihar Osun.

Saidai wani shafi a Twitter wanda yake ikirarin shi daya daga cikin wadanda ake nema ne yace damfarar dala $20 kawai yayi aka kamashi.

Yace amma a aikawa Mahaifiyarsa Miliyan 5 din da aka ce an saka akan duk wanda ya taimaka aka kamasu shi kuma zai koma gidan yarin da kansa.

Saidai wasu na shakkun cewa ba shi bane.

Karanta Wannan  YANZU-YANZU: Shugaba Bola Ahmed ya isa birnin Tokyo na kasar Japan Gabannin taron TICAD na 2025, Ambasada Hideo MATSUBARA, jakadan Japan mai kula da TICAD ya tarbe shi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *