
Gwamnan jihar Katsina da ke arewacin Najeriya ya ayyana yau Juma’a a matsayin ranar hutu ga ma’aikata domin “tarɓar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu” da ke ziyara a jihar tasu.
Gwamna Dikko Radda ya bayyana hakan ne ranar Alhamis yayin jawabin da ya gabatar a taron Ranar Ma’aikata.
“Ina mai farin cikin shaida muku cewa Shugaba Tinubu zai kawo ziyara Katsina gobe [Juma’a] domin buɗe ayyuka da dama da muka kammala cikin shekara biyu da suka wuce,” in ji gwamnan.
“Saboda haka, na ayyana goben a matsayin ranar hutu saboda ma’aikata su samu damar haɗuwa da mu wajen tarɓar shugaban ƙasa.”
A jiya Alhamis ne fadar shugaban Najeriya ta sanar cewa Tinubu na jam’iyyar APC zai kai ziyarar aiki ta kwana biyu a jihar da ke arewa maso yamma kuma ta tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.