Thursday, March 26
Shadow

Gwamnatin tarayya ta kwace mukamin Jakadancin data baiwa Usman Nasamu Dakin Gari

A daren jiyane dai gwamnatin tarayya ta bayyana Usman Nasamu Dakin gari a matsayin jakadan Najeriya a kasar Turkiyya.

Saidai a yau da Safiyar Juma’a, Gwamnatin ta bayyana kwace wannan mukami.

Zuwa yanzu dai ba’a bayyana dalilin Gwamnatin na kwace wannan mukami ba.

Duka sanarwar nadashi da kwace mukamin ta fito ne daga bakin me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga.

Ana tsammanin nan ba da jimawa ba, shugaba Tinubu zai kai ziyara kasar ta Turkiyya.

Karanta Wannan  Dan Datti Baba Ahmad me jami'ar Base University dake Abuja ya kammala karatu daga jami'ar Landan, Lamarin ya jawo cece-kuce

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *