Thursday, February 5
Shadow

Gwamnatin Tarayya zata biya bashin Naira Tiriliyan 2 na kudin wutar lantarki

Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta fara amincewa da batun biyan bashin Naira Tiriliyan 2 na wutar lantarki da akw binta.

Hakan kokarine na samar da ingantacciyar wutar Lantarki a Najeriya.

Na kusa da me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar makamashi, Eriye Onagoruwa ce ta bayyana hakan a wajan wani taron masu ruwa da tsaki na harkar wutar da aka gudanar.

Tace gwanatin na duba muhimmancin hakan wajan samar da wutr Lantarki me karfi. Inda tace gwamnatin na kokarin ganin ta samar da wata hanya ta bashi dan biyan wannan bashi musaman lura da karancin kudin da gwamnatin ke fama dashi.

Karanta Wannan  DA ƊUMI-ƊUMI: Wata budurwa ta fito kan titi dauke da allo inda take shaidawa Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf cewa ta gama karatu amma ba aiki, ta ce harakar kwamfuta ta karanta amma duk aikin da aka bata tana so

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *