Thursday, February 26
Shadow

ICPC ta maka tsohon kwamishinan El-Rufai a kotu

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa da sauran laifuka masu alaƙa ta Najeriya ICPC ta maka kwamishina a tsohuwar gwamnatin Nasir El-Rufa’i na jihar Kaduna, Bashir Saidu a kotu bisa zargin almundahanar kuɗi.

Jami’in shari’a na hukumar ICPC, Osuobeni Akponimisingha ne ya gabatar da ƙarar a babbar kotun tarayya da ke Kaduna a ranar Talata, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Takardar ƙarar mai lamba FHC /KD/IC/ 2025, ta nuna cewa an maka Bashir Sa’idu a kotun ne bisa tuhume-tuhume guda biyu da suka danganci almundahana da rashawa.

A wani rahoto da majalisar dokokin jihar Kaduna ta fitar a bara, ta zargi tsohuwar gwamnatin da almundahanar sama da naira biliyan 423 na jihar.

Karanta Wannan  Hotunan dan shekaru 60 daya nemi auren 'yar shekaru sha shida sun dauki hankula, wasu dai sun ce kudi gareshi shiyasa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *