Friday, January 17
Shadow

ICPC ta maka tsohon kwamishinan El-Rufai a kotu

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa da sauran laifuka masu alaƙa ta Najeriya ICPC ta maka kwamishina a tsohuwar gwamnatin Nasir El-Rufa’i na jihar Kaduna, Bashir Saidu a kotu bisa zargin almundahanar kuɗi.

Jami’in shari’a na hukumar ICPC, Osuobeni Akponimisingha ne ya gabatar da ƙarar a babbar kotun tarayya da ke Kaduna a ranar Talata, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Takardar ƙarar mai lamba FHC /KD/IC/ 2025, ta nuna cewa an maka Bashir Sa’idu a kotun ne bisa tuhume-tuhume guda biyu da suka danganci almundahana da rashawa.

A wani rahoto da majalisar dokokin jihar Kaduna ta fitar a bara, ta zargi tsohuwar gwamnatin da almundahanar sama da naira biliyan 423 na jihar.

Karanta Wannan  Ya kamata Gwamnonin Arewa su canja matsaya akan kin amincewa da kudirin dokar Haraji da Shugaba Tinubu ya kawo,abu ne me kyau da zai karawa gwamnati hanyar kudaden shiga>>Inji Sanata Shehu Sani

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *