
Jam’iyyar PDP ta yi martani kan komawar Gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori zuwa jam’iyyar APC.
Shugaban jam’iyyar na riko, Ambassador Umar Damagum, ya bayyana cewa sun tafi kotu da neman Gwamna Sheriff ya sauka daa kujerar Gwamna tunda a karkashin PDP aka zabeshi.
Yace a baya sun fuskanci matsalolin da suka fi wannan yawa kuma duk sun tsallake dan haka wannan wasan yara ne.
Yace an baiwa Gwamnatin gudanarwa na yankin kudu maso kudu umarnin ya kula da jam’iyyar PDP a jihar ta Delta saboda duka ‘yan jam’iyyar a jihar sun canja sheka.