Friday, December 5
Shadow

Kada Ki Kuskura Ki Sake Shigowa Majalisa, Gargaɗin ‘Yan Majalisar Dattaawa Ga Sanata Natasha, Bayan da tace ranar Talatar nan zata koma majalisar

Kada Ki Kuskura Ki Sake Shigowa Majalisa, Gargaɗin ‘Yan Majalisar Dattaawa Ga Sanata Natasha

Daga Muhammad Kwairi Waziri

A wata sabuwar sabani da ke kara dagula lamura a Majalisar Dattawa, wani sashe na majalisar ya fitar da gargadi mai zafi ga Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, inda suka ce:

“Kar ki kuskura mu ga ƙafarki a majalisar dattijai domin har yanzu ki na ƙarƙashin dakatarwarmu.”

Wannan gargadi na zuwa ne kwanaki bayan Sanata Natasha ta sanar da shirinta na komawa kujerarta a majalisar ranar Talata mai zuwa. Majalisar ta nuna cewa akwai hukuncin dakatarwa da har yanzu ba a janye ba, kuma duk wani yunkuri nata na komawa za a ɗauka a matsayin sabawa doka da ka’ida.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Ministan Tsaro, Muhammad Badaru ya sauka daga mukaminsa inda ya bayar da dalilin rashin Lafiya

Sai dai har yanzu ba a fitar da cikakken bayani daga ofishin shugaban majalisar kan ainihin dalilin dakatarwar ko matakin da za a ɗauka idan ta bayyana a zauren majalisa ba.

A halin yanzu, ana sa ran wannan sabanin zai janyo cece-kuce a tsakanin magoya bayanta da masu riko da tsarin majalisa, musamman ganin cewa Natasha na daya daga cikin sanata mata da suka fito da karfi a zaɓen 2023.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *