Friday, January 9
Shadow

Kalli Bidiyo: A karshe dai Tauraruwar fina-finan Hausa, Khadija MaiNumfashi ta fito daga hannun ‘yansanda inda tace fhadanta da Marwat ya kare

Tauraruwar fina-finan Hausa, Khadija MaiNumfashi ta sanar da fitowarta daga hannun ‘yansanda bayan da aka kamata.

Tace Kabiru Legas ne ya je wajan ‘yansanda yace an yiwa rayuwarsa barazana inda aka tambayeshi wa yake zargi yace ita yake zargi.

Tace dan haka dole ne yasa aka kirata amma Allah ya wanke ta.

A karshe ta yi godiya ga masoyanta da abokan sana’arta da ‘yan uwa bisa irin soyayyar da aka nuna mata.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Ummi Nuhu ita ta jawa kanta duk irin halin da aka ganta a ciki>>Inji Mistin Besty, Ya fallasa irin abinda ya sani akanta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *