Thursday, February 26
Shadow

Kalli Bidiyo Da Duminsa: Dandanzon jama’ar da Rotimi Amaechi ya tara a jihar Rivers yayin da ya kai ziyara ofishin jam’iyyar ADC na jihar

Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi ya kai ziyara ofishin jam’iyyar ADC a jihar Rivers.

Tun a filin jirgin sama na jihar ya fara tara mabiyansa inda suka masa rakiya zuwa ofishin jam’iyyar ADC.

A jawabinsa, yace jiharsu ta saba da rubuta sakamakon zabe ba tare da la’akari da kuri’un mutane da aka kada ba.

Yace dolene a dakatar da hakan.

Amaechi na daga cikin gamayyar ‘yan Adawa da suka fice daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar ADC.

Karanta Wannan  Ji Yanda 'yansanda suka yi ta maza suka kashe Habu Dan Damisa duk da kokarin hanasu da wasu masu kumbar susa suka yi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *