Friday, July 17
Shadow

Kalli Bidiyo Da Duminsa: Dandanzon jama’ar da Rotimi Amaechi ya tara a jihar Rivers yayin da ya kai ziyara ofishin jam’iyyar ADC na jihar

Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi ya kai ziyara ofishin jam’iyyar ADC a jihar Rivers.

Tun a filin jirgin sama na jihar ya fara tara mabiyansa inda suka masa rakiya zuwa ofishin jam’iyyar ADC.

A jawabinsa, yace jiharsu ta saba da rubuta sakamakon zabe ba tare da la’akari da kuri’un mutane da aka kada ba.

Yace dolene a dakatar da hakan.

Amaechi na daga cikin gamayyar ‘yan Adawa da suka fice daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar ADC.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Baana ya fito ya kira sunan matar Rarara, Aishatulhumaira ya bata hakuri bayan da ta kaishi ofishin DSS

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *