Sunday, July 13
Shadow

Kalli Bidiyo: ‘Yan Shi’a sun koka kan cirewa matansu hijabi da ‘yansanda suka yi a Abuja

Kungiyar ‘yan uwa musulmi da aka fi sani da shi’a aun koka kan cirewa matansu Hijabi da ‘yansanda suka yi a Abuja.

Kungiyar tace wannan cin zarafine da kuma batanci ga addinin musulunci.

Wakiliyar mata ta kungiyar ‘yan uwa musulmi, Maryam Sani ta bayyana a wata sanarwa data fitar cewa zasu yadawa duniya wannan lamari a gani.

Kuma zasu kai maganar kotu.

Bidiyo dai ya bayyana a kafafen sada zumunta inda aka ga ‘yansanda na cirewa matan ‘yan shi’ar Hijabi ta karfin tsiya.

Karanta Wannan  Ban yi wata murna sosai da zama shugaban kasa ba, saboda irin barnar da na iske n yiwa Najeriya>>Tinubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *