
Wani me suna Inusa Sa’idu yayi ikirarin cewa a Musulunci aka haifeshi.
Yace amma daga baya yayi Mafarki da Jesus yana ce masa ya tafi coci inda yace dalili kenan yayi ridda inda a yanzu ma shi malami ne a kiristanci.
Ya bayyana hakane a wani Bidiyonsa daya watsu sosai a kafafen sada zumunta.
A wani sashe na Bidiyon nasa, an ganshi yana karatun Qur’ani dan ya tabbatarwa da mutane cewa shi Musulmi ne a da.