
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya dawo daga kasar Egypt inda ya hadu da barazanar kame daga DSS a filin jirgi bayan da ya sauka a Najeriya.
Saidai El-rufai yaki yadda yabi DSS din inda yace idan suna son gayyatarsa su aiko masa da takarda.
Ya bayyana cewa ko shugaban kasa, bai isa yace masa ga abinda ya kamata yayi ba.
Jama’a da yawa sun taru suka hana a tafi da malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda suka ce sai ya je gida.
A karshe, me magana da yawunsa, Muyiwa Adejobi ya bayyana cewa, DSS sun kwace fasfon ElRufai din.