
Bayan kalaman da Naja’atu ta yi akan Farfesa Isa Ali Pantami inda ta bayyanashi da makaryaci lamarin ya dumama kafafen sada zumunta.
Wani Bidiyo ya bayyana inda aka ji Farfesa na cewa, Allah ne kadai zai yabi mutum ya daukaka ko kuma ya aibatashi ya kaskanta.
Farfesa ya kara da cewa, idan mutum ya ga dama ya shiga BBC yayi ta zaginsa bai dameshi ba.
Duk da be kama suna ba, da yawa sun fassara cewa, Martanine yawa Naja’atu.