
Cece-kuce ya barke a kafafen sada zumunta bayan da Malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi yace aje Idi kuma aje Sallar Juma’a.
Malam yace idan ya zamana mutum daya zai je to ya je Juma’a ya bar Idi.
Saidai bayan bayyanar wannan jawabi nasa, An rika yada tsohon Bidiyon Marigayi, Dr. Idris Dutsen Tanshi inda ya bayar da fatawar cewa idan mutum yayi Idi, ba lallai yayi Juma’a ko Azahar ba.