
Babban Malamin Addinin Islama kuma tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa, Sheikh Isa Ali Pantami ya bayyana cewa, yana cikin wadanda suka taimakawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ci zabe.
Yace kuma shine ya yi Addu’a ya shafa a jikin shahadar nasarar zabe da INEC ta baiwa Tinubu.
Hakanan yace, Shugaba Tinubu mukamai 3 ya bashi amma duk yaki karba yace akwai abinda ya saka a gaba.
Malam ya bayyana hakane yayin da ya je ofishin jam’iyyar APC dan sabunta rijistarsa ta jam’iyya.