
Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa wasu tsagera sun bi fastocin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun lalatasu a fadin jihar.
Sakataren yada labarai na jihar, Malam Yusuf Idris ne ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai.
Yace wannan cin fuskane wanda ba zasu yadda dashi ba inda yayi kira ga jami’an tsaro su dauki mataki kan lamarin.