Thursday, February 26
Shadow

Ku daina sauraren karairayin kafafen sada zumunta ku goyi bayan shugaba Tinubu>>Wike ya gayawa Mutanen Abuja

Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya nemi mutanen Abuja da su daina sauraren karairayin da ake musu a kafafen sada zumunta.

Hakanan yace su daina sauraren ‘yan Adawa wadanda kansu ba a hade yake ba.

Ya bayyana hakane a wajan kaddamar da wani titi a Apo.

Inda yace a baya karairayi kawai ake musu amma a yanzu gashi ana fada da cikawa.

Wike ya jawo hankalinsu da su goyi bayan Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dan shine ya musu aiki na zahiri.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon rikici Huijsen da Lamine Yamal da ya dauki hankula a daren jiya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *