Wednesday, April 8
Shadow

Kungiyar dattawan Yarbawa ta Afenifere ta yi kira ga shugaba Tinubu da ya gaggauta amincewa da kafa ‘yansandan Jihohi

Kungiyar dattawan Yarbawa ta Afenifere ta yi kira ga shugaba kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya gaggauta amincewa da kafa ‘yansandan jihohi.

Kungiyar ta bayyana hakane bayan taro na masu ruwa da tsaki da ta yi a gidan shugabanta, Chief Reuben Fasoranti dake Akure.

Ta yi kira ga shugaban kasar da ya fitar da kudirin doka wanda zai bayar da damar canja kundin tsarin mulkin Najeriya dan a samar da ‘yansandan Jihohi inda tace ya aika da wannan kudirin dokar zuwa majalisa.

Hakan na kunshene a cikin sanarwar da sakataren yada labaran Kungiyar, Jare Ajayiya fitar inda yace sun yaba da kokarin Gwamnati na magance matsalar tsaro amma akwai bukatar a kara himma.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Wasu 'yan kudu na ta shan ruwan Allah wadai bayan da suka samu wani me sayar da Balangu yana Sallah, suka rika yankar naman da yake sayarwa suna ci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *