Wednesday, March 18
Shadow

Matatar man Dangote ta kori duka ma’ikatanta na Najeriya bayan da suka shiga kungiyar kwadago ta PENGASSAN

Rahotanni sun ce matatar man fetur ta Dangote ta kori duka m’aikatanta ‘yan Najeriya.

Matatar tace ta yi hakanne dan canja fasalin ayyukanta.

Saidai hakan na zuwane bayan da ma’aikatan suka shiga kungiyar kwadago ta ma’aikatan man fetur ta PENGASSAN.

Jimullar wadanda aka kora daga aikin sun kai mutane 1000 saidai matatar bata kori ma’akatan dake mata aiki ‘yan kasashen waje ba.

Rikici da rashin fahimtar juna yai kamari tsakanin Dangote da kungiyar ta PENGASSAN inda ta zargi Dangoten da hana ma’aikatan matatarsa shiga kungiyar wanda tace hakan ya sabawa dokokin aiki a Najeriya.

Saidai Dangote ya sha cewa shiga kungiyar kwadagon zabine ba abune na dole ba.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon wani matashi daga jihar Katsina na fadin cewa, bai taba samun farin ciki irin na gwamnatin Tinubu ba, Yace da mata daya gareshi yanzu ya kara, hakanan kasuwarsa ta habaka kuma matsalar 'yan Bìndìgà ta gushe a karamar hukumarsa ta Jibia

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *