
Tsohon shugaban kamfanin mai na kasa, NNPCL, Mele Kolo Kyari ya fito ya karyata rade-radin da ake yadawa cewa wai yana hannun hukumar EFCC inda ake bincikensa.
Kyari ya fitar da sanarwa ta shafinsa na X inda yace a yanzu yana hutawa ne bayan kammala yiwa Najeriya aiki na tsawon shekaru 34.
Yace a lokacin da yake aiki ko hutun sati biyu baya samu dan haka yanzu yana hutun da ya kamata ace yayi a baya.
Yace ‘yan uwa da abokan arziki suna ta kiranshi suna sanar dashi game da wani labari dake cewa an kamashi yana hannun EFCC.
Yace wannan labari karyane, yace a sanda yake aiki ya sa Allah a ransa saboda yasan zai tsaya a gaban Allah ya amsa tambayoyi.
Dan haka yace a yanzu ma a shirye yake ya amsa tambayoyin EFCC ka yanda ya gudanar da ayyukansa.
Yace ya kamata a daina yada irin wannan labari dan kuwa ba zaiwa masu zuba jari ko masu son zuba jari a Najeriya dadi ba.
Yace ya kamata kafafen yada labarai su rika tantance labari kamin su yadashi.