
Shugaban kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu ya bayyana cewa ba da son ransa ya dawo Najeriya, garkuwa dashi aka yi.
Ya bayyana hakane a yayin zaman kotu dake sauraren kararsa.
Yace kuma shi ya kafa kungiyar ESN ne dan su baiwa iyayensu dake shiga daji kariya ba dan su kaiwa kowa hari ba.
Da aka tambayeshi game da hare-haren da aka kai kan jami’an tsaro da sauran hukumomin Gwamnati, Nnamdi Kanu yace bai san da wannan ba dan shi baya tayar da Fitina.