Thursday, December 18
Shadow
Babu kasar data kai Najeriya dadi, kada ku je ku ki dawowa, Shugaba Tinubu ya gayawa Kiristoci masu shirin tafiya Jerusalem dan aikin ibada

Babu kasar data kai Najeriya dadi, kada ku je ku ki dawowa, Shugaba Tinubu ya gayawa Kiristoci masu shirin tafiya Jerusalem dan aikin ibada

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gargadi kiristoci masu son tafiya jeru salem Ibada cewa kada wanda ya makale a can yaki dawowa Najeriya. Shugaban yace babu kasar data kai Najeriya 'yanci da dadi musamman idan mutum na zaune a wata kasar ba bisa ka'ida ba. Shugaban ya bayyana hakane ta bakin Sakataren Gwamnatin tarayya, Sanata George Akume a yayin da kiristocin ke shirin tafiya aikin ibadar.
Karya ake min ban ce zan baiwa Yarbawa fifiko ba idan na zama shugaban kasa>>Atiku Abubakar

Karya ake min ban ce zan baiwa Yarbawa fifiko ba idan na zama shugaban kasa>>Atiku Abubakar

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa, ba gaskiya bane labarin da yake yawo cewa wai yace zai baiwa yarbawa kulawa da mukamai na musamman idan ya zama shugaban kasa. Atiku yace wanda ya fitar da sanarwar da yawunsa me suna Kola Johnson be sanshi ba. Atiku ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawunsa Paul Ibe. Inda ya bukaci a yi watsi da wannan magana.
Kalli Bidiyon: Duk da cewa kudin Tarihin Duniya yace ba ruwansa da shiriritarta, Matashiyarnan mara Kunya ‘yar Legas tace ba zata fasa ba, sai ta yi Alfasha da maza 100

Kalli Bidiyon: Duk da cewa kudin Tarihin Duniya yace ba ruwansa da shiriritarta, Matashiyarnan mara Kunya ‘yar Legas tace ba zata fasa ba, sai ta yi Alfasha da maza 100

Duk Labarai
Matashiyar nan marar kunya ta jihar Legas, Ayomiposi Oluwadahunsi wadda aka fi sani da Mandy Kiss tace duk da kundin tarihin Duniya yace ba zai karrama ta ba idan ta yi lalata da maza 100, ba zata fasa ba. Tace tuni ta sayi fakiti na kwandam inda take gayyatar maza zuwa Ikorodu. Tace ko da mutum ba zai yi ba, tana gayyatarsa ya je ya sha kallo. Ta bayyana cewa dai a watan Oktoba ne zata aikata wannan masha'a saidai bata fadi sunan wajan da zata aikata hakan ba. https://twitter.com/Teeniiola/status/1970723550521893060?t=_QdTAUIMpixvtqGHkHOeLA&s=19 https://twitter.com/Teeniiola/status/1971143834601132165?t=1bukeNydE-hM6KU_yjWQ1g&s=19
Duk da rage farashin man fetur da Dangote yayi, gidajen mai har yanzu suna sayarwa a tsohon farashi me tsada

Duk da rage farashin man fetur da Dangote yayi, gidajen mai har yanzu suna sayarwa a tsohon farashi me tsada

Duk Labarai
Rahotanni sun ce har yanzu gidajen man fetur na sayar da man a farashi me tsada duk da rage farashin da matatar man fetur ta Dangote ta yi. A makon daya gabata ne Matatar man ta sanar da rage farashin daga Naita 865 zuwa naira 820 akan kowace lita musamman tace saboda tankokin man ta 1000 zasu fara jigilar man zuwa gidajen mai kyauta. Saidai binciken da jaridar Punchng ta yi yace har yanzu a jihohin Legas da Ogun da sauran wasu jihohi gidajen man basu fara sayar da man a sabon farashi ba.
Wata Sabuwa: Marigayi tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na daga cikin wadanda suka aikawa matar shugaban kasa, Remi Tinubu da tallafi na murnar zagayowar ranar Haihuwarta, wanda a yanzu kudin sun haura Naira Biliyan 20

Wata Sabuwa: Marigayi tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na daga cikin wadanda suka aikawa matar shugaban kasa, Remi Tinubu da tallafi na murnar zagayowar ranar Haihuwarta, wanda a yanzu kudin sun haura Naira Biliyan 20

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Marigayi tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na daga cikin wadanda suka aikawa matar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, Watau Remi Tinubu da tallafin data nema na zagayowar ranar Haihuwarta. Remi Tinubu ta nemi a tara mata kudi a yayin data cika shekaru 65 da haihuwa inda tace za'a yi amfani da kudin wajan kammala ginin hedikwatar dakin karatu na kasa. Tuni aka sanar cewa kudin sun kai sama da Naira Biliyan 20 wadanda 'yan Najeriya suka tara mata. Saidai wani abin mamaki shine, cikin jerin mutanen da suka tura mata da kudaden tallafin hadda tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari. Hakan na zuwane duk da cewa, tun kamin Uwargidan shugaban kasar ta fara neman wannan tallafin Buhari ya rasu. Abin ya zowa mutane da yawa da mamaki matuka. ...
Bariki ba dadi, Gidan iyaye yafi dadi, Dan Allah ku daina zagin mu, ku rika mana Addu’a mu da muka fito daga gidan iyayen mu muka shiga bariki, Allah ya shiryemu>>Inji A’isha Beauty

Bariki ba dadi, Gidan iyaye yafi dadi, Dan Allah ku daina zagin mu, ku rika mana Addu’a mu da muka fito daga gidan iyayen mu muka shiga bariki, Allah ya shiryemu>>Inji A’isha Beauty

Duk Labarai
A'isha Beauty ta bayyana cewa, Gidan iyaye yafi dadi. Ta bayyana hakane a shafinta na sada zumunta inda tace masu zaginsu, su da suka baro gidan iyayensu suka shiga bariki su daina. Ta yi rokon a rika musu addu'ar Allah ya shiryesu. Ta kuma yiwa masu shirin barin gidan iyayensu su shiga bariki addu'ar Allah ya karkatar da zuciyarsu zuwa daidai. https://www.tiktok.com/@aysha.beauty50/video/7553099428987555080?_t=ZS-901OilwIYxF&_r=1