Thursday, September 3
Shadow

Bai kamata ace an nada Tsohon Shugaban INEC da ya sauka mukamin Jadaka ba, ni dai da nine shugaban kasa ba zan yi haka ba>>Inji Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa bai kamata shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya nada tsohon shugaban INEC jakada ba

Yace hakan zai sa wasu su yi zargin cewa watakila ya taimakawa Tinubun da magudin zabene shine yake saka masa da mukamin Jakada

Yace shi dai da shine shugaban kasa ba zai aikata hakan ba.

Farfesa Mahmoud Yakubu tsohon shugaban hukumar zabe me zaman kanta INEC na daga cikin sunayen da shugaba Tinubu yake son baiwa mukamin jakadanci.

Karanta Wannan  Daya daga cikin 'yan majalisar Amurka da ke Zuga Trump akan Najeriya na shan suka bayan da yace Garin da aka yi Gharkuwa da 'yan mata 'yan Makaranta a jihar Kebbi garin Kiristane

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *