Tuesday, December 16
Shadow
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara jihar Kaduna, Gobe Juma’a

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara jihar Kaduna, Gobe Juma’a

Duk Labarai
Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu zai kai ziyara jihar Kaduna a gobe, Juma'a idan Allah ya kaimu. Shugaban zai halarci daurin auren dan Sanata Abdulaziz Yari me suna Nasirudeen Yari da amaryarsa, Safiyya Shehu Idris. Hakan na kunshene a cikin wata sanarwa da me magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar a ranar 18 ga watan Satumba. Hakanan sanarwar tace shugaban kasar zai kuma kaiwa matar tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari ziyara. Sannan a Ranar Juma'ar dai ne shugaban zai koma Abuja.
Atiku Abubakar ya hadu da Nafisa Abdullahi data lashe gasar Turanci ta Duniya, ya ce ya dauki nauyin karatunta

Atiku Abubakar ya hadu da Nafisa Abdullahi data lashe gasar Turanci ta Duniya, ya ce ya dauki nauyin karatunta

Duk Labarai
Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya ce ya gana da Nafisa Abdullahi wadda ta lashe gasar Turanci ta Duniya. Yace ganawar ta kasance a gidansa dake Abuja insa yace ya dauki nauyin karatunta dana sauran wanda suka ci yo gasar tare. Hakan na zuwane bayan da aka ga daliban an basu kyautar naira dubu dari biyu a ma'aikatar ilimi ta tarayya
Kalli Bidiyon ganawar mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima da wani Inyamuri da suka yi magana da Hausa, Abin ya dauki hankula

Kalli Bidiyon ganawar mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima da wani Inyamuri da suka yi magana da Hausa, Abin ya dauki hankula

Duk Labarai
Bidiyon Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima a wani gidan mai tare da wani Inyamuri ya dauki hankula. A Bidiyon an ji Kashim Shettima na magana da mutumin da Hausa inda yake ce masa babu maganar Biafra kuma babu wanda zai koreshi daga Arewa. https://twitter.com/masuzafi/status/1968580980609798564?t=Ry_c8NdIQeG2Xo8ha2VMLQ&s=19
Gwamnatin Najeriya ta mayar da darasin tarihi a firamare da sakandare

Gwamnatin Najeriya ta mayar da darasin tarihi a firamare da sakandare

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta sake mayar da darasin tarihi a matsayin darussan dole da ɗalibai za su dinga yi makarantun firamare da sakandare na ƙasar. Wata sanarwa da ma'aikatar ilimi ta fitar a ranar Laraba ta ce an ɗauki matakin ne domin "ƙarfafa kishi, da haɗin kai tsakanin 'yan ƙasa". "A karon farko ɗaliban Najeriya za su fara yin darasin tarihi tun daga aji 1 na firamare zuwa aji 3 na ƙaramar sakandare [JSS3], yayin da 'yan aji 1 zuwa 3 [SS1 zuwa SS3] za su dinga yin darasin ilimin rayuwa da tsatso [Civic and Heritage Studies]," in ji sanarwar da ta wallafa a shafukan zumunta. "'Yan aji 1 zuwa 6 na firamare za su san asalin Najeriya, da gwanayenta, da shugabanni, da al'adu, da siyasa, da addini, da mulkin mallaka, da kuma mulki bayan samun 'yancin kai. "Ɗaliban JSS1-3 za su naza...
Kalli Bidiyon yanda aka gano irin abinda larabawa manyan masu kudi kewa ‘yan Matan da ake kaiwa Dubai da sunan yin aiki

Kalli Bidiyon yanda aka gano irin abinda larabawa manyan masu kudi kewa ‘yan Matan da ake kaiwa Dubai da sunan yin aiki

Duk Labarai
Wani bincike da BBC ta yi ya gano yanda ake kai 'yan mata daga Afrika Dubai suna karuwanci. Binciken yace ba karuwanci kadai ake kai 'yan matan yi ba, hadda ci musu zarafi ta hanyar yin futsari da kashi a jikinsu. Hakan ya fara fitowa fili ne tun bayan da wata da aka kai ta yi irin wannan abu tace ba zata yi ba inda ta kwammace ta fado daga Bene ta mutu. Daya daga cikin irin wadannan 'yan matan da aka kai da aka yi hira da ita tace ko sun kira 'yansanda basa daukar wani mataki akan lamarin. BBC tace ta yi kokarin tuntubar 'yansandan amma basu bata hadin kai ba. https://www.tiktok.com/@abis_fulani/video/7551156980916751638?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7551156980916751638&source=h5_m&tim...
Shoprite sun kulle shagunansu a Ibadan da Ilorin, saboda mutane basa zuwa siyayya, Hakanan a shagunan Abuja da Legas na Shoprite ba kaya saboda matsin tattalin arziki

Shoprite sun kulle shagunansu a Ibadan da Ilorin, saboda mutane basa zuwa siyayya, Hakanan a shagunan Abuja da Legas na Shoprite ba kaya saboda matsin tattalin arziki

Duk Labarai
Rahotanni sun ce Kamfanin manyan shagunan siyayya na Shoprite ya kulle a Ilorin da Ibadan saboda matsin tattalin arziki da ya hana mutane zuwa siyayya. Hakanan a Abuja da Legas, Shagunan na Shoprite ba kaya. Hakannna zuwa ne saboda matsin tattalin arziki da Najeriya ke fama dashi. A baya dai Shoprite sun kulle shagonsu dake Kano.
Kalli Bidiyo: Ina da Otal mutane suka daina zuwa, shine na mayar dashi gidan Qaruwai, a yanzu ina samun dubu dari 3 duk rana

Kalli Bidiyo: Ina da Otal mutane suka daina zuwa, shine na mayar dashi gidan Qaruwai, a yanzu ina samun dubu dari 3 duk rana

Duk Labarai
Wani me otal da yace mutane sun daina zuwa kama daki a otal dinsa, yace ya mayar da otal din gidan karuwai. Yace wani abokinsa ne ya bashi shawara kuma shawarar ta yi aiki. Yace amma matarsa tace ba zata zauna ta raini 'ya'yansu da kudin da aka samu daga gidan karuwai ba. Yace yayi-Yayi da ita takiya ta tafi gidansu, kuma tace ba zata dawo ba sa ya kulle gidan karuwan. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1968381354888020150?t=5aijlnagtqVXRDui1ypOWg&s=19
Mun raba kudin Talli Naira Biliyan 330 ga gidaje Miliyan 8.5 a Najeriya>>Inji Ministan kudi

Mun raba kudin Talli Naira Biliyan 330 ga gidaje Miliyan 8.5 a Najeriya>>Inji Ministan kudi

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya tace ta rabawa gidaje Miliyan 8.5 Tallafin kudi Naira Biliyan 330 a fadin Najeriya. Ministan kudi, Wale Edun ne ya bayyana hakan. Ya bayyana hakane ranar Laraba a Abuja inda yace gwamnati ta dawo da raba tallafin bayan Gyare-Gyaren da aka wa tsarin. Yace suna raba kudadenne saboda ragewa mutane radadin tsadar rayuwa inda yace mutane Miliyan 15 suke son rabawa. Yace zuwa yanzu sun raba kudin a gide Miliyan 8.5 inda suke biyan Naira dubu shirin da biyar duk wata. Ministan yace sauran ma zuwa karshen shekarar nan za'abasu.
Kalli Bidiyo: Shekarata 30 da haihuwa kuma aurena 9>>Inji Wannan Tauraruwar fina-finan Hausan

Kalli Bidiyo: Shekarata 30 da haihuwa kuma aurena 9>>Inji Wannan Tauraruwar fina-finan Hausan

Duk Labarai
Tauraruwar Fina-finan Hausa ta bayyana cewa Shekarunta 30 kuma aurenta 9. Ta bayyana hakane a yayin wata ganawa da aka yi da ita inda tace auren na 9 be dade da mutuwa ba. Tace a baya, bata iya fadin haka amma yanzu zata iya fada ko dan ya zamarwa wasu darasi. https://www.tiktok.com/@mustaphayalo/video/7550385904641182994?_t=ZS-8zp8RqburxJ&_r=1