Gwamnatin Kano ta jaddada aiwatar da dokar hana sana’ar achaɓa a jihar
Gwamnatin jihar Kano ta sanar da jaddada aiwatar da dokar hana sana'ar achaɓa ta shekarar 2013, wani mataki da ta ce zai taimaka wajen kare tsaro da rage laifuka, da tabbatar da doka da oda a fadin jihar.
Ma’aikatar Shari’a ta bayyana cewa dokar, wadda ta dade tana nan daram kuma za a ci gaba da aiwatar da ita sosai.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar da babban mai bai wa gwamnan jihar Shawara Kan Harkokin Labarai na Ma’aikatar Shari’a ya fitar
Babban lauyan jiharkuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru Maude, SAN, ya buƙaci jama’a musamman masu baburan haya wata acaɓa da su yi biyayya ga tanade-tanaden dokar.
Ya tunatar da cewa “Dokar ba sabuwa ba ce, kuma dole a kiyaye ta domin amfanin kowa da kowa.”
A cewarsa, gwamnatin jihar ba za ta lamunci karya dokar ba, mus...








