Yayin da Dalibai Kiristoci ke zargin an hanasu gona coci a jami’o’in Kashere, Gombe dana BUK, Kano, Shima wani dalibi musulmi yayi zargin cewa an hana Musulmai gina masallaci a jami’ar Jos, UniJos
A dazu ne hutudole ya kawo muku rahoton yanda wasu Kiristoci dalibai daga jami'o'in BUK, Kano da Kashere, Gombe inda suke zargin an hanasu gina coci a wadannan makarantu yayin da aka bar musulmai suka gina masallatai.
A martani ga wannan zargi shima wani dalibi musulmi yai zargin cewa an hana dalibai musulmai gina masallaci a jami'ar UNIJos, dake jihar Filato.
Yace duk da akwai masalacin da aka fara ginawa amma an hana a karasashi.
Sannan yayi zargin cewa an ma hana musulmai yin salla a masallacin da ba'a karasa ba.
https://twitter.com/Abdul_Ahmad_/status/1995361298482385141?t=uxPj8rW8-jvRmbak-pY-BA&s=19








