Sunday, May 25
Shadow
Hukumar NCC ta gano mutum 1 me layukan waya dubu dari(100,000) a Najeriya

Hukumar NCC ta gano mutum 1 me layukan waya dubu dari(100,000) a Najeriya

Duk Labarai
Hukumar kula da sadarwa,NCC ta bayyana cewa ta gano wani mutum 1 wanda ke da layukan waya dubu dari (100,000) shi kadaai. Wakilin Hukumar, Reuben Muoka ne ya bayyana hakan inda ya jaddada cewa ranar 14 ga watan Satumba me zuwa ne rana ta karshe ga kowa ya hada layinsa da lambar NIN. Yace suna aiki ne tare da ofishin Babban me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu dan dakile barazanar tsaro. Sannan yace suna aiki tukuru dan hana sayar da layukan wayar da aka riga aka musu rijista.
Abin a Yaba: Ya tsinki Dala $10,000 kwatankwacin Naira Miliyan 15 a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano ya mayarwa mesu

Abin a Yaba: Ya tsinki Dala $10,000 kwatankwacin Naira Miliyan 15 a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano ya mayarwa mesu

Duk Labarai
Wani ma'aikacin filin jirgin sama a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano me suna Auwalu Ahmed Dankade ya tsinci dala $10,000 kwatankwacin Naira Miliyan 15 amma ya mayar da ita ga maishi. Auwalu Ahmed Dankade yanawa wani kamfanin kula da karbar sako aiki ne a filin jirgin saman kjma a hirarsa da Daily Trust ya bayyana cewa iyayensa sun masa tarbiyyar kada ya dauki duk wani abu da ba nashi ba, ya wadata da abinda Allah ya bashi. Kamfanin da yakewa aiki dake Legas,ya gayyaceshi zuwa Legas din inda ake tsammanin za'a girmamashi ne.
Mun baku wata daya ku sauko da farashin kayan abinci ko mu daureku>>Gwamnatin Tarayya ga ‘yan kasuwa

Mun baku wata daya ku sauko da farashin kayan abinci ko mu daureku>>Gwamnatin Tarayya ga ‘yan kasuwa

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta hannun hukumar dake kula da tsaftar gasa a kasuwanci da kiyaye hakkokin masu sayen kaya, FCCPC ta baiwa 'yan kasuwa wata daya su karya farashin kayansu ko su dandana kudarsu. sabon shugaban hukumar, Mr. Tunji Bello ne ya bayyana haka a wajan wani taro na masu ruwa da tsaki ranar Alhamis daya gudana a Abuja. Yace bayar da misalin wani lemu da ake sayarwa a kasar amurka akan $89 wadda yace kwatankwacin Naira 140,000 ne amma a wani babban shagon sayayya dake Legas sun ga ana sayar da lemun akan Naira 944,999. Yace wannan yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa ne wanda kuma ba zasu lamunta ba. Yace duk wanda aka kama akan wannan laifi zai iya fuskantar tara me yawa ko kuma dauri.
Ji Martanin da Hadiza Gabon tawa wani da yace mata ta bashi kudi

Ji Martanin da Hadiza Gabon tawa wani da yace mata ta bashi kudi

Duk Labarai, Hadiza Gabon
Tauraruwar Fina-finan Hausa, Hadiza Gabon ta wallafa wannan hoton nata a shafinta na sada zumunta inda masoyanya suka rika yabawa. Saidai wani ya roketa da ta yiwa mutane kyautar kudi kamar yanda dan siyasa na jihar Kaduna,Bello ElRufai ke yi. Saidai Hadizar ta mai martanin cewa, ya je ya samu aikin yi. Ya dai mayar mata da martanin cewa, ko ya kawo takardunsa ta bashi aiki a dakin hada shirye-shiryenta na Youtube? Daga nan dai Hadizar bata sake takashi ba. A baya dai, Abokiyar aikin Hadizar, Rahama Sadau ta rabawa masoyanta kudade ta shafukan sada zumunta na Facebook da Instagram.

Jimullar ‘yan Najeriya 55,910 ne aka kashe an kuma yi garkuwa da 20,000

Duk Labarai
Wata kungiya dake saka ido akan harkokin tsaro ORFA ta bayyana cewa daga shekarar 2019 zuwa 2023 an samu kashe mutane 55,910 da yin garkuwa da guda 20,000. Kungiyar tace kungiyoyin IS-WA-P da B0k0 Haram ne da takwarorinsu suka yi wadannan aika-aika. A ranar Alhamis ne kungiyar ta fitar da wannan bayani inda tace amma kiristoci ne suka fi fuskantar wannan matsala. Wakilin Kungiyar, Frans Vierhout ya bayyana cewa hakan ya nuna yanda lamuran tsaro suka tabarbare a Najeriya.
ABIN ALFAHRI: Matashi Dan Arewa Na Farko Da Ya Kammala Karatu A Fannin Magungunan Musulunci A Kasar Qatar

ABIN ALFAHRI: Matashi Dan Arewa Na Farko Da Ya Kammala Karatu A Fannin Magungunan Musulunci A Kasar Qatar

Duk Labarai
ABIN ALFAHRI: Matashi Dan Arewa Na Farko Da Ya Kammala Karatu A Fannin Magungunan Musulunci A Kasar Qatar. Dakta Muhammadu Kabiru Hassan (Dangwamna) dake Samaru Zaria ya zama mutum na farko da ya fito daga yankin Arewacin Nijeriya da ya kammala karantu a kasar Qatar National Museums Authority bangaren islamic herbal medicine curse. Daga karshe ya nemi jama'a da su yi masa addu'ada fatan alkairi, Allah Ya sa karatun da ya yi ya amfani muśùĺùñci gaba daya.