Friday, December 19
Shadow
Jam’iyyar LP ba za ta shiga kowace ƙawance ba a 2027

Jam’iyyar LP ba za ta shiga kowace ƙawance ba a 2027

Duk Labarai
Jam'iyyar adawa ta LP a Najeriya ta nesanta kanta daga shiga kowace irin ƙawance dmin tunkarar zaɓen 2027. Kwamitin zartarwar jam'iyyar ƙarƙashin jagorancin Julius Abure ne ta tababtar da haka lokacin wani taro da ta gudanar a Abuja, babban birnin ƙasar. A baya-bayan nan dai jam'iyyun hamayya a Najeriya na ta ƙoƙarin ƙulla wata haɗaka domin tunkarar jam'iyyar APC mai mulki a zaɓen 2027. To sai dai jam'iyyar ta LP ta ce ba za ta shiga kowace irin haɗaka. “Taronmu a jajjada cewa jam'iyyarmu ba ta ciki, kuma ba za ta shiga kowane irin haɗaka ba domin tunkarar zaɓen 2027, a maimakon haka jam'iyyar LP za ta mayar da hankali wajen sake gina kanta ta hanyar ɓullo da sabbin sadaru da ƙarfafa kanta domin samun nasara a zaɓen 2027'', in ji Abure.
Saudiyya ta saka tarar riyal 20,000 ga masu yin aikin Hajji ba bisa ƙa’ida ba

Saudiyya ta saka tarar riyal 20,000 ga masu yin aikin Hajji ba bisa ƙa’ida ba

Duk Labarai
Ma'aikatar harkokin cikin gida ta Saudiyya ta tabbatar da cewa duk mutumin da aka kama yana taimaka wa mutane wajen yin aikin Hajji ba bisa ƙa'ida ba zai fuskanci tarar riyal 100,000. Tarar za ta shafi duk wanda da ke ɓoye maniyyatan da ba su da cikakkun takardu a gidajensu, ko nema musu biza, ko kuma yin jigilarsu. Lokutan da dokokin suka shafa su ne daga 1 ga watan Zulƙi'ida (wanda ya yi daidai da 29 ga watan Afrilu) har zuwa 14 ga watan Zulhijja (10 ga watan Yuni). Duk mutumin da aka kama yana ƙoƙarin gudanar da aikin Hajjin ba tare da takardun izini ba zai fuskanci tarar riyal 20,000. Sannan kuma za a mayar da shi ƙasarsa tare da hana shi shiga Saudiyya tsawon shekara 10. Irin wannan tarar za a yi wa duk wanda aka kama da kowace irin biza ta ziyara wadda ta gama aiki yan...
Duka kwalejojin ilimi a Najeriya za su fara ba da shaidar digiri

Duka kwalejojin ilimi a Najeriya za su fara ba da shaidar digiri

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta ce ta fara aiwatar da sabon tsarin Dual Mandate Policy a dukkan kwalejojin ilimi na ƙasar wanda ke ƙunshe cikin sabuwar dokar kwalejojin ilimi ta 2023. A cewar wata sanarwa daga ma'aikatar ilimi, dokar ta bai wa dukkan kwalejojin damar bayar da shaidar karatu ta digiri da kuma NCE a lokaci guda a fannin koyarwa. Ministan Ilimi Tunji Alausa ya siffanta tsarin a matsayin "babba kuma na cigaba". "Wannan tsari na Dual Mandate Policy ba gyara ba ne kawai, gagarumin sauyi ne da ke bai wa kwalejojin damar bayar da shaidar NCE da kuma digiri," in ji ministan kamar yadda sanarwar ta ruwaito. "Tsarin zai ƙarfafa kwalejojin, ya ƙara yawan damar samun ilimi, kuma ya kyautata ingancin azuzuwan koyarwa a faɗin Najeriya."
Ana Zargin Abokan Dan Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Jama’are, Isa Wabi Da Kašhè Shi A Yayin Da Suka Hauro Masa Gida Cikin Darè A Jihar Bauchi

Ana Zargin Abokan Dan Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Jama’are, Isa Wabi Da Kašhè Shi A Yayin Da Suka Hauro Masa Gida Cikin Darè A Jihar Bauchi

Duk Labarai
Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Bauchi ta ce ta kama mutum ɗaya bisa zargin kashe tsohon shugaban ƙaramar hukumar Jama'are Isa Wabi. A cewar wata sanarwa da rundunar ta fitar a yau Juma'a, waɗanda ake zargin abokan ɗansa ne kuma sun aikata kisan ne da tsakar daren yau a gidansa da ke Fadaman Mada. Nan take aka kai shi asbitin Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa bayan rahoto ya ishe 'yansandan cewa wasu matasa sun caccaka masa wuƙa a wuya. "Binciken farko-farko ya nuna wasu mutum biyu ne suka aikata kisan waɗanda abokan ɗan Wabi ne ɗan shekara 24 mai suna Abdulgafar Isa Mohammed," a cewar sanarwar. Ta ce dakaru sun tarar da ɗaya daga cikin mutanen a sume kuma aka kai shi asibiti, inda daga baya aka tabbatar da mutuwarsa. 'Yansanda sun ce sun kama Abdulgafar domin ci gaba...
Ƙungiyar Kiristoci ta CAN Ta Nemi Haɗin Gwiwar Shiga Ayyukan Hisbah, Don Magance Baɗala

Ƙungiyar Kiristoci ta CAN Ta Nemi Haɗin Gwiwar Shiga Ayyukan Hisbah, Don Magance Baɗala

Duk Labarai
Ƙungiyar CAN Ta Nemi Haɗin Gwiwar Shiga Ayyukan Hisbah, Don Magance Baɗala Daga Mustapha Abubakar Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) ta nemi haɗin gwiwa da kuma samun cikakken damar shigar da membobinta cikin ayyukan hukumar Hisbah domin samun kyakkyawar dangantaka da haɗin kai a aiki. Fasto Nuhu Sani, Sakataren CAN na ƙaramar hukumar Sabon Gari a jihar Kaduna, ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron bita na kwana ɗaya da hukumar Hisbah ta shirya a sakatariyar ƙaramar hukumar. Fasto Sani ya ce tun da hukumar Hisbah ƙungiya ce ta addini da ke da alhakin kawar da miyagun ayyuka a cikin al’umma, ya zama dole a samu haɗin gwiwa da ƙungiyar Kiristoci domin cika wannan buri. Sakataren ya lurantar da cewa Musulmai da Kiristoci suna zaune tare a wuri ɗaya, a don haka ya zama ...
An Kama wani Ɗan Nijar a Dajin Yankari sanye da kayan sojoji.

An Kama wani Ɗan Nijar a Dajin Yankari sanye da kayan sojoji.

Duk Labarai
An Kama wani Ɗan Nijar a Dajin Yankari sanye da kayan sojoji. Rundunar ‘yan sandan Bauchi ta kama wani mutum mai suna Jibrin Ali, ɗan shekara 28 daga Zandar, Jamhuriyar Nijar, a cikin dajin Yankari da ke ƙaramar hukumar Alkaleri. An kama shi ne yayin sintiri na hadin gwiwa, yana sanye da kayan sojoji, kuma ana zargin yana ciki waɗanda suke tada hankali a yankin wanda ya ke fama da ayyukan ‘yan bindiga, ya kasa bayar da sahihin bayani kan dalilin kasancewarsa a dajin.Kwamishinan ‘yan sanda ya bada umarnin a gudanar da cikakken bincike.
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya alƙawarta samar wa sojojin ƙasar kayan aiki domin fatattakar ayyukan ƴanbindiga a arewacin ƙasar.

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya alƙawarta samar wa sojojin ƙasar kayan aiki domin fatattakar ayyukan ƴanbindiga a arewacin ƙasar.

Duk Labarai
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya alƙawarta samar wa s5ojojin ƙasar kayan aiki domin fatattakar ayyukan ƴanbindiga a arewacin ƙasar. Yayin da yake jawabi ga sojojin ƙasar ranar Juma'a a wata ziyara da ya kai jihar Katsina - ɗaya daga cikin jihohin da ke fama da ayyukan ƴan fashin daji, shugaban ƙasar ya ce matsalar ƴanta'adda da masu garkuwa da mutane da ƴan fashin daji ta jima a ƙasar. "Ƴan Najeriya sun zuba muku ido, suna jiran ku kawo ƙarshen matsalar tsaro tare da ƙwato kowane yanki na ƙasarmu, ku nuna wa maƙiyan Najeriya cewa ƙaryarsu ta ƙare'', in ji Shugaba Tinubu. ''Gwamnati na ɗaukar matakan samar muku isassun kayan aiki, da suka haɗ da sabbin fasahohin zamani da sabbin hanyoyin tattara bayanan sirri da dabarun yaƙi, ba wai don kare ƙasarmu kaɗai ba, sai don samun ƙar...