Dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar Labour party a zaben shekarar 2023, Peter Obi ya kaiwa tsohon ministan shari'a, Abubakar Malami ziyara a ofishinsa.
Wadannan hotunane daga ganawarsu, babu dai karin bayani kan abinda suka tattauna.
Ba a cire Atiku a matsayin Wazirin Adamawa ba — Gwamnatin Adamawa.
Gwamnatin Jihar Adamawa ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen yada labarai cewa ta cire tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, daga sarautar Wazirin Adamawa.
A baya-bayan nan, gwamnatin jihar ta fitar da wata sanarwa da ke bayyana cewa mutanen da ke masarautar su ne kaɗai ke da hakkin naɗa basarake da mambobin majalisar masarauta.
Wannan sabon tsarin ya sa kafafen yada labarai da dama suka fassara cewa an cire Atiku daga matsayin Wazirin Adamawa.
Amma a wani taron manema labarai da aka gudanar a jiya Laraba, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare na Jihar Adamawa, Iliya James, ya bayyana cewa wannan sabon tsarin bai cire kowa daga mukaminsa ba.
Ya kuma ƙara da cewa duk wasu sabbin shirye-s...
2027: Idan Tinubu ya bani takarar mataimakin shugaban ƙasa da gudu zan karɓa - Barau Jibrin.
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya bayyana cewa ko da yake ba ya son ya shiga cikin muhawarar wanda zai iya zama abokin takarar Shugaba Bola Tinubu a 2027, zai karɓi kowane nau’in aiki da Shugaban ƙasa zai danka masa cikin farin ciki da biyayya.
Yayin wani taron manema labarai da aka shirya dangane da shirin jin ra’ayoyin jama’a a shiyyoyi daban-daban da Kwamitin Majalisar Dattawa kan Sauya Kundin Tsarin Mulki , Barau ya ce: “Duk abin da Shugaba ya bukace ni da in yi, zan yi shi dari bisa dari ”
Wannan bayani na zuwa ne bayan wata magana da ya yi a ranar Talata, inda ya shawarci wata ƙungiya da ke goyon bayan kudurin sa ya zama mataimakin shugaban kasa a 202...
An kama malamar makaranta me suna Sarah Jacas saboda batawa dalibinta me shekaru 14 tarbiyya.
Rahotanni sun ce malamar takan yi lalata da dalibin nata har a cikin aji sau da yawa.
Kuma sukan yi Chatin inda takan aika masa da sakon cewa tana sonshi.
Lamarin ya farune a makarantar Corner Lake Middle School dake Florida ta kasar Amurka.
A yaune shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sanyawa dokar canja fasalin Haraji hannu.
Shugaban ya sakawa dokar hannu a fadarsa wanda lamarin ya samu halartar kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio da takwaransa na majalisar wakilai, Tajudeen Abbas da wasu gwamnoni da sauran manyan ma'aikatan Gwamnati.
Sabuwar dokar harajin dai a cewar shugaban zata kawo ci gaba sosai a kasarnan har ga wadanda ba'a haifa ba.
Wata mata me shekaru 46 da bata taba aure ba ta koka da cewa maza na gudunta suna cewa ta tsufa.
Tace yawanci mazan dake zuwa wajanta mazan aurene kuma ba aure ke kaisu wajanta ba, suna nemanta da lalata ne.
Tace da yawa idan suka ganta sai su ce ta tsufa.
Ta koka da cewa ba ita kadai bace a wajan mahaifiyarta ba amma ita kadai ce bata yi aure ba.
Matar tace wallahi bata taba sanin Namiji ba, kuma idan mutum na da yanda zai gwada, yana iya gwadawa ya gani.
Ta bayyana hakane a wata hira da aka yi da ita a wani gidan rediyo me suna Agidigbo FM inda tace tana neman taimakon a samo mata mijin aure.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sanya hannu kan sababbin dokokin haraji huɗu a wani mataki na sauya fasalin tsarin karɓa da tattara haraji na ƙasar.
Gwamnatin ta ce sabbin dokokin za su sauƙaƙa tsarin, da rage wahalhalun haraji kan ɗaiɗaikun mutane da kamfanoni, da kuma taimakawa wajen inganta karɓar haraji.
"Sauye-sauyen za su taimaki masu ƙaramin ƙarfi tare da tallafa wa ma'aikata ta hanyar ƙara yawan abin da suke samu,'' kamar yadda Shugaba Tinubu ya bayyana a watan da ya gabata lokacin bikin cika shekara biyu a kan mulki.
Ya ƙara da cewa: "Sauye-sauyen sun cire muhimmman abubuwa kamar abinci da ilimi da kula da lafiya daga tsarin biyan harajin VAT. Haka nan, sabon tsarin ya keɓe karɓar rance da sufuri da makamashin da ba ya gurɓata muhalli, duka wadannan ba za su biya harajin...