Tuesday, December 16
Shadow
Mun kusa fara biyan alawus ɗin naira 77,000 – NYSC

Mun kusa fara biyan alawus ɗin naira 77,000 – NYSC

Duk Labarai
Hukumar NYSC ta ce ta kusa fara biyan masu yi wa ƙasa hidima alawus ɗin naira 77,000. Hukumar ta bayyana haka ne a matsayin martani kan rashin fara biyan sabon alawus ɗin bayan an sanar da ƙari daga naira 33,000 da ake biya biyo bayan ƙara mafi ƙanƙantar albashi. A watan Yulin shekarar da ta gabata ne gwamnatin tarayya ta yi alƙawarin fara biyan sabon alawus ɗin, amma har yanzu ba a fara biya ba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito daga masu bautar ƙasar. A watan Janairu, darakta-janar na NYSC, Birgediya-janar Yushau Ahmed ya sanar da cewa daga watan Fabrairu za a fara biyan sabon alawus ɗin, amma kuma ba a biya ba a watan na Fabrairu da ya gabata. Daraktan riƙo na hulɗa da jama'a na hukumar, Caroline Embu, ta ce suna jiran kuɗi ne da umarni kafin fara biyan sa...
Darajar wasu kuɗaɗen kirifto ta tashi bayan sanarwar Donald Trump

Darajar wasu kuɗaɗen kirifto ta tashi bayan sanarwar Donald Trump

Duk Labarai
Darajar wasu kuɗaɗen kirifto sun tashi bayan shugaba Donald Trump ya sanar da cewa za a kafa wani rumbun adana kuɗaɗen kirifto na ƙasar Amurka. Ya ambaci kuɗin kirifto na Bitcoin da Ethereum da XRP, da ADA SOL a cikin wani jawabi da ya yi a kafofin sadarwa, inda ya ƙara da cewa Amurka ce za ta zama babbar cibiyar hada-hadar kirifto ta duniya. Jim kaɗan da yin jawabin ne darajar kuɗaɗen da ya ambata suka tashi, inda Bitcoin da Etherium suka ƙara daraja da kusan kashi 10 kafin suka ja baya, sannan sauran kuɗaɗen ma suka tashi. A baya dai Trump da matarsa Melania sun fitar da kuɗinsu na kirifto na matakin meme.
Hukumar EFCC tace itace ta kai samame Otal a Jihar Naija ba ‘yan Bìndìgà ba

Hukumar EFCC tace itace ta kai samame Otal a Jihar Naija ba ‘yan Bìndìgà ba

Duk Labarai
A jiyane dai muka samu rahoton cewa, 'yan Bindiga cikin shiga irin ta EFCC sun kai samame wani otal dake Chanchanga inda suka sace mutane 10. Saidai a yau, hukumar EFCC ta fito inda ta bayyana cewa, itace ta kai wannan samame ba 'yan Bindiga ba. Hukumar ta wallafa a shafinta na yanar gizo cewa, ta samu bayanai akan wasu 'yan damfarar yanar gizo ne dake zaune a otal din inda wakilanta na jihar Kaduna suka kai samame kan otal din me suna WhiteHill Hotel dake Chanchaga a jihar ta Naija. Sanarwar tace an kama mutane 11 daga otal din sannan hukumar tace ta gudanar da aikinta cikin kwarewa da bin doka dan haka bata san daga inda maganar 'yan Bindiga ta samo asali ba. Hakanan kuma sanarwar tace an kwace motoci 2 da wayoyin hannu 13. Sanarwar tace za'a gurfanar da wadanda ake zargin...
Kalli Bidiyo yanda aka wulakanta wani barawon Kunin Aya inda aka sashi yace shi barawo ne ya saci kunun aya

Kalli Bidiyo yanda aka wulakanta wani barawon Kunin Aya inda aka sashi yace shi barawo ne ya saci kunun aya

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wannan wani mutum ne da aka kama a wani Shago a Abuja ya saci kunin Aya. Bayan kamashi an sashi ya rike takardar da ta ce ni barawo ne na saci kunun aya. https://www.youtube.com/watch?v=EFI6pOhuVsc Daga baya dai an barshi ya tafi ba'a masa komai ba. Mutanene suka roki me shagon ya kyaleshi.
Bai kamata ka turo matarka ta rika fada da Natasha ba, kai ya kamata ka tsaya a yi da kai>>Betty Akeredolu

Bai kamata ka turo matarka ta rika fada da Natasha ba, kai ya kamata ka tsaya a yi da kai>>Betty Akeredolu

Duk Labarai
Matar marigayi tsohon gwamnan jihar Ondo, Betty Akeredolu ta bayyana cewa bai kamata kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya saka matarsa a cikin fadan da suke da Sanata Natasha Akpoti ba. Tace kamata yayi ace ya tsaya an yi fadan dashi ba ya koma gefe ya turo matarsa ba. Betty ta bayyana hakanne a kafar X. Tace kuma Sanata Natasha Akpoti ta birgeta data fito ta nuna rashin jin dadinta kan canja mata kujera ba tare da saninta ba. Tace dan an yiwa wasu sun yi shiru hakan ba yana nufin itama ta yi shiru bane. tace irin su Sanata Natasha Akpoti ne ya kamata ace mata suna sakawa a gaba dan su jagorancesu musamman a majalisa.
Alawus din da kuke dauka me yawa da yanda kukafi kowa kudi na baiwa ‘yan Najeriya haushi sosai>>Batist Church ta gayawa Tinubu

Alawus din da kuke dauka me yawa da yanda kukafi kowa kudi na baiwa ‘yan Najeriya haushi sosai>>Batist Church ta gayawa Tinubu

Duk Labarai
Kungiyar Baptist church dake Abuja sun caccaki gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda suka bukace shi yayi wani abu game da yunwa da matsin rayuwa dake damun 'yan Najeriya. Cocin ta bayyana hakane a yayin taron cikarta shekaru 10 da kafuwa a Abuja inda manyan baki a wajan suka soki irin rayuwar kece raini da 'yan siyasa ke yi yayin da su kuma talakawa aka barsu cikin halin kaka nikayi. Daya daga cikin wadanda suka yi magana a wajan taron zhine Reverend Dr. Israel Akanji inda yayi kira ga gwamnati data kawo tallafi a bangaren Ilimi, da lafiya da noma. Yace 'yan Najeriya da yawa na daf da fadawa matsalar yunwa da zata iya kaisu ga halaka. Yace suna yabawa da kokarin da gwamnati take yi amma akwai bukatar a kara kaimi. Yace Alawus masu yawa da 'yan siyasa ke dauka da kum...
Barayi sun sace mashina 3 yayin da ake sallar Taraweeh a Abuja

Barayi sun sace mashina 3 yayin da ake sallar Taraweeh a Abuja

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Barayi sun sace mashina 3 a wani masallaci dake Tipper garage dake Kuje, babban Birnin tarayya, Abuja. Lamarin ya farune ranar Asabar a yayin da ake sallar Taraweeh a wani masallaci dake cikin Gidan mai. Wani shaida me suna Ibrahim Jamilu ya bayyanawa jaridar Daily Trust cewa, bayan sun kammala sallah, mutane 3 sun bayyana cewa, an sace musu mashina. Yace sun sanar da kungiyar masu mashina da kungiyar 'yan Kato da Gora wanda aka bazama neman mashinan. Saidai 'yansandan dake yankin sunce ba'a sanar dasu ba.
Jam’iyyar APC a jihar Kebbi ta dakatar da Kabir Sani-Giant saboda kai maciji cikin gidan gwamnatin jihar ya tsorata mutane

Jam’iyyar APC a jihar Kebbi ta dakatar da Kabir Sani-Giant saboda kai maciji cikin gidan gwamnatin jihar ya tsorata mutane

Duk Labarai
Jam'iyyar APC a jihar Kebbi ta dakatar da Kabir Sani-Giant saboda kai maciji cikin gidan Gwamnatin jihar ya tsorata mutane. Sakataren Jam'iyyar na jihar, Alhaji Sa’idu Muhammad-Kimba ne ya fitar da wannan sanarwa a ranar Lahadi. Yace ranar February 8, 2025 Kabir ya shiga da maciji cikin gidan gwamnatin jihar inda ya tsorata mutane, yace hakan ya sabawa kundin tsarin Jam'iyyar. Yace dakatarwar da akawa kabir zata ci gaba da zama har zuwa lokacin da za'a kammala buncike akansa.