Saturday, December 20
Shadow
Da Duminsa: Majalisar Tarayyar Najeriya ta nemi a canja tsarin mulki da zai baiwa shugaban kasa damar yin zango daya na shekaru 6

Da Duminsa: Majalisar Tarayyar Najeriya ta nemi a canja tsarin mulki da zai baiwa shugaban kasa damar yin zango daya na shekaru 6

Siyasa
Wasu 'yan majalisar wakilai sun nemi cewa, a canja tsarin mulkin Najeriya da zai baiwa shugaban kasa damar yin mulki na shekaru 6 wa'di daya. Sannan sun nemi a rika yin karba-karbar mulki tsakanin yankuna 6 da ake dasu a kasarnan. Dan majalisar daga jihar Imo, Ikenga Ugochinyere ne ya bayyana hakan inda yace idan shugaban kasa, Gwamnoni suka rika yin wa'adi daya na shekaru 6 kawao, za'a samu saukin kashe kudi da kuma yin aiki me kyau.
DA ƊUMI-ƊUMI: An yanke wa magoya bayan Valencia su uku ɗaurin wata 8 bisa nuna wariyar launin fata a kan Vinicious Junior na Real Madrid.

DA ƊUMI-ƊUMI: An yanke wa magoya bayan Valencia su uku ɗaurin wata 8 bisa nuna wariyar launin fata a kan Vinicious Junior na Real Madrid.

Real Madrid, Vinicius Jr
An yanke wa magoya bayan Valencia su uku ɗaurin wata 8 bisa nuna wariyar launin fata a kan Vinicious Junior na Real Madrid. Tun a cikin watan Mayu ne su ka nuna wa ɗan wasan gaban na Madrid da Brazil wariyar launin fata. Sky Sports News ta rawaito cewa wannan shi ne karo na farko da aka taba hukunta masu nuna wariyar launin fata a kan ƴan wasa a Spain.
A wannan satin ake sa ran Manchester United zata kori Ten Hag

A wannan satin ake sa ran Manchester United zata kori Ten Hag

Kwallon Kafa, Labaran Manchester United
A wannan satin da muke ciki ake sa ran Kungiyar Manchester United zata kori me horas da 'yan wasanta Erik Ten Hag. Thomas Tuchel ne dai ake tsammanin zai maye gurbin Ten Hag a matsayin sabon kocin United. Tuni kuma har Thomas Tuchel ya gana da wakilin Manchester United, Sir Jim Ratcliffe Tuchel ya bayyana cewa idan aka bashi aikin horas da Manchester United, zai dawo da Jadon Sancho zai kuma yi aiki da Mason Mount.
PDP Ta Sanya Ranar Da Za ta Yi Taron NEC Karo Na Biyu

PDP Ta Sanya Ranar Da Za ta Yi Taron NEC Karo Na Biyu

Siyasa
PDP Ta Sanya Ranar Da Za ta Yi Taron NEC Karo Na Biyu Jam’iyyar PDP ta bayyana ranar Alhamis 26 ga watan Satumba a matsayin ranar da za ta gudanar da taron majalisar zartarwa ta kasa karo na biyu a shekarar 2024. Idan za a iya tunawa, a taron farko da hukumar NEC ta gudanar a ranar 18 ga watan Afrilu,an tattauna batutuwan da suka hada da makomar mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Ambasada Illiya Damagum, an daga shi zuwa taron NEC na gaba wanda aka shirya tun watan Agusta. Kungiyar ‘yan jam’iyyar ta Arewa ta tsakiya ta ce za a zabi dan takara daga shiyyar don kammala wa’adin tsohon shugaban Jam'iyyar na kasa, Dr. Iyiorchia Ayu, wanda ya yi murabus kusan shekaru biyu cikin wa'adinsa na shekaru hudu. Gabanin taron NEC na watan Satumba, jam’iyyar ta tsayar da ranar 27 ga wata...
Aikin Hajji: Karin Wani Mahajjacin Daga Jihar Kebbi Ya Rasu A Makkah

Aikin Hajji: Karin Wani Mahajjacin Daga Jihar Kebbi Ya Rasu A Makkah

Hajjin Bana
Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kebbi ta sanar da rasuwar wani Mahajjacin jihar a birnin Makkah na kasar Saudiyya. Hakan ya fito ne a cikin wata sanarwa da kungiyar yada labarai ta Kebbi Hajj 2024 ta fitar a ranar Lahadi. Shugaban hukumar Alhaji Faruku Aliyu-Enabo ya bayyana sunan marigayin da Abubakar Abdullahi wanda ya fito daga Gulma a karamar hukumar Argungu. A cewar Aliyu-Enabo, Abdullahi ya rasu ne bayan gajeruwar rashin lafiya. Shugaban hukumar ya bayyana cewa Gwamna Nasir Idris ya nuna alhininsa kan rasuwar tare da yi wa marigayin addu’a, inda ya roki Allah ya gafarta masa kurakuransa, ya kuma ba shi Jannatul Firdaus. “Gwamnan ya kuma bukaci iyalan mamacin da abokan arziki da mahajjatan Kebbi da su jajirce wajen karbar nufin Allah Madaukakin Sarki cikin aminci,” i...
ƳANZU-YANZU: Za a fassara huɗubar Arfa da Hausa, Cewar Sheikh Sudais

ƳANZU-YANZU: Za a fassara huɗubar Arfa da Hausa, Cewar Sheikh Sudais

Siyasa
Babban Limamin Masallatan Harami Sheikh Abdurrahman Sudais ya sanar cewa za a fassara hudubar Ranar Arafa kai-tsaye a cikin harshen Hausa da wasu harsuna 19 domin karuwar alhazai da sauran al'ummar Musulmi a fadin duniya. Sheikh Sudais ya ce ana sa ran sama mutum miliyan 100 za su saurari hudubar wadda Sheikh Maher Al Mu'ayqaly zai gabatar a Masallacin Namirah ta kafofin watsa labarai daban-daban.
Da Duminsa: Kungiyar Kwadago, NLC ta yi watsi da tayin Naira dubu suttin da biyu(62,000) ta bayyana ranar da zata ci gaba da yajin aiki

Da Duminsa: Kungiyar Kwadago, NLC ta yi watsi da tayin Naira dubu suttin da biyu(62,000) ta bayyana ranar da zata ci gaba da yajin aiki

Siyasa
Kungiyar Kwadago, NLC ta bayyana cewa bata akince da tayin Naira dubu 62 a matsayin mafi karancin Albashi ba. Tace kai ko dubu 100 ba zata amince dashi a matsayin mafi karancin Albashin ba, Kungiyar tace wannan kudi sun yi kadan wa ma'aikata su rayu ciki rufin asiri. Mataimakin babban sakataren kungiyar, Chris Onyeka ne ya bayyana haka a Channels TV yayin ganawa dashi ranar Litinin. Ya kuma ce kwaki 7 ko sati daya da suka baiwa gwamnati kan ta bayyana matsayinta ya kare ranar Talata, kuma idan gwamnatin ta dage akan hakan, zasu sake zama ranar talatar dan tsayar da matsaya kan ci gaba da yajin aikin. “Our position is very clear. We have never considered accepting N62,000 or any other wage that we know is below what we know is able to take Nigerian workers home. We will not nego...

Yadda mace zata motsa sha awar mijinta

Auratayya, Ilimi, Sha'awa
Mataki na farko wajan motsa sha'awar miji shine ya zamana ya ci abinci ya koshi, ki tabbatar a koshe yake kamin maganar tada sha'awa. Ya zama baya cikin tashin hankali, ko da yana cikin tashin hankali, ki bari zuciyarsa ta yi sanyi kamin maganar tada sha'awa, ko kuma kina iya farawa da kalaman sanyaya rai. Saka riga me sharara ba tare da Rigar noni ba ko dan kamfai watau Pant. Kina iya sakata kina gittawa ta gabansa ko kuma ki zauna kusa dashi. Ya zamana kina kanshi, watau jikinki na kanshi, gidan ma na kanshi hakanan gidan da dakinku duka a tsaftace. Kina iya ce masa ku zo ku yi rawa, Ki kunna muku waka kuna rawa, kina juya masa duwawu, daidai mazakuatarsa. Idan kuma ba me son rawa bane, ku yi wasa, ki ce ya goyaki ko kuma ku yi wasan tsere, ko na buya da sauransu. Kina iya...