Friday, December 5
Shadow

Qhasar Amurka ta zhargi Sarkin Musulmi da hannu wajan Muzhghunawa Kirista

Tsohon Magajin garin Blanco City dake jihar Texas a kasar Amurka, Mike Arnold ya zargi me alfarma sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III da hannu wajan kisan kiyashi da aikata Jihadiy akan Kiristoci.

Ya bukaci sarkin da ya fito ya kawo hujja wadda ke nuna cewa bashi da hannu a khiysan da akewa Kiristoci a Arewa.

Saidai fadar sarkin ta bayyana cewa wannan zargi ne da bashi da tushe ballantana makama.

Sannan tace ba zata ma bayar da amsa ba game da zargin.

Sakataren fadar, Alhaji Saidu Maccido, yace Gwamnatin tarayya da Majalisar tarayya sun bayar da amsa kan wannan lamari dan haka hankalin sarki akan karfafa zaman lafiya yake ba irin wadannan maganganun ba.

Karanta Wannan  Dattawan Yarbawa sun ja kunnen shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kan fifiko da yake nunawa wajan baiwa Yarbawa mukamai da yawa fiye da sauran kabilun kasarna

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *