Sunday, March 16
Shadow

Sai mun hada kai da ‘yan kudu dan ceto Najeriya daga halin da take ciki>>El-Rufai

Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, sai Arewa ta hada kai da ‘yan kudu dan ceto Najeriya daga halin data tsinci kanta.

El-Rufai ya bayyana hakane a yayin ziyarar gaisuwar da ya kai Jihar Delta ta gaisuwar mutuwar Edwin Clark.

El-Rufai wanda tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar yawa jagora zuwa jihar Delta yace Arewa ta sha hada kai da kudu dan cimma burikanta na siyasa.

Karanta Wannan  Cire tallafin Man fetur ne abu mafi kyau da armashi da ya faru da Najeriya>>Inji Sanata Sani Musa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *