Tuesday, June 3
Shadow

Sanata Natasha Akpoti ta kasa kawo hujjar cewa na nemeta da lalata shiyasa ta fara bani Hakuri, kumama inda zaku san sharri ne irin nasu na mata ta kulla min, bayan tace ne nemeta da lalata ta bini min je taruka da yawa har kasashen waje kuma har hotunan Selfie ta rika dauka dani>>Sanata Godswill Akpabio

Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya bayyana cewa Sanata Natasha Akpoti ta kasa kawo hujjojin kan zargin da take masa na cewa, ya nemeta da lalata.

Ya bayyana hakane ta bakin lauyansa, Dr Olisa Agbakoba (SAN) yace dalili ma kenan na yin magamganin da ta yi kwanannan.

Yace wani karin abin mamaki shine, Sanata Natasha Akpoti ta goge rubutun da ta yi na zargin da take masa a shafinta na sada zumunta.

Yace wani karin abin dubawa shine Sanata Natasha Akpoti tace a shekarar 2023 ne Ya nemeta da lalata, amma bayan nan, ta bishi sun je taruka da yawa a ciki da wajen Najeriya a shekarar 2024.

Karanta Wannan  An kama Fasto da yin mu'ujizar karya inda yace ya mayar da wata mata me kudi amma sai bayan kwanaki aka ganta tana sayar da Lemun Kwalba

Yace a wajan wasu tarukan ma har hotunan Selfie take daukarsu tare kuma ta dora a kafafen sadarwa.

Dan haka ya nemi Sanata Natasha Akpoti ta janye zargin da take masa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *