
Shugaban Kungiyoyin gwagwarmaya da suka hada kai suka kai bukatar a binciki tsohon shugaban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL, Mele Kolo Kyari ya je ya janye bukatar binciken.
Kungiyoyin sun ce basa tare da shugaban nasu me suna Kabir Matazu.
A wata sanarwa da sakataren kungiyoyin me suna Moses Okino ya fitar, yace Matazu ya yaudaresu da cin amanarsu.
Kungiyar tace dama can akwai wasu na hannun damar Mele Kolo Kyari dake ta son su hana binciken me gidan nasu.
Yace dan haka abinda Matazu yayi ba da yawun kungiya yayi ba yayi ne shi kadai bisa radin kansa.
Yace Matazu bai tuntubesu ba dan haka suna kyautata zaton kudi aka bashi.