Thursday, March 19
Shadow

Tsageran ESN Sun kashe sojojin Najeria biyu daya ya bace, sun kuma tsere da makaman sojojin

Hukumar sojojin Najeriya ta tabbatar da mutuwar sojojin ta 2 bayan harin da kungiyar ESN dake karkashin kungiyar IPOB ta kai mata.

A sanarwar data fitar ranar Asabar, Hukumar sojojin ta bayyana cewa, lamarin ya farune a garin Osina dake karamar hukumar Ideator ta Arewa dake jihar Imo a yayin da wata tawagar sojojin ke dawowa daga wani dauki da suka kai a yankin Osina bayan kiran da aka musu cewa kungiyar ta ESN ta kai hari garin.

Hakanan sanarwar tace sojojin sun fafata da ESN a yankin Nkwachi inda suka kashe mutum daya daga ciki sauran suka tsere sannan kuma an kwato bindiga daya aga hannunsu.

Karanta Wannan  INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Sama Da Mutàñe Gomà Suñ Ŕasù Sakamakòn Wani Hadaŕi Da Ya Auku A Garin Okène Dake Jihar Kogi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *