Sunday, August 23
Shadow

Tsaka Mai Wuya: Har yanzu Atiku yaƙi karɓar katin zama ɗan Jam’iyyar ADC kan jin Jonathan zai koma PDP

Tsaka Mai Wuya: Har yanzu Atiku yaƙi karɓar katin zama ɗan Jam’iyyar ADC kan jin Jonathan zai koma PDP

Tsohon Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar yaƙi ya karɓi katin zama ɗan Jam’iyyar ADC, a yayinda ake ci gaba da jita-jitar cewa tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan zai yi takara a shekarar 2027.

Atiku, wanda a ƴan kwanakin baya ya fita daga jam’iyyar PDP bayan ɗaukar tsawon lokaci ana rigingimu, an tsara zai karɓar katin jam’iyyar ADC.

Atiku dai zai karɓi katin jam’iyyar ADC a garin sa na Jada da ke ƙaramar hukumar Jada ta Adamawa, an tsara cewa zai karɓi katin jam’iyyar a ranar Laraba 6 ga watan Agusta, amma aka ɗage karɓar katin ba tare da wani bayani ba.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Na yadda da mijina dari bisa dari, kai ko ce min kika yi ga mijina can a gidan Qaruwai, zan ce miki wa'azi ya je musu>>Inji Wannan matar

Daga Usman Salisu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *